-
AU Ta Jajantawa Kasashe Mambobinta Sanadin Rasa Rayuka A Ambaliyar Ruwa
Aug 24, 2017 11:41Kungiyar tarayyar Afrika (AU) ta jajantawa kasashe mambobinta bisa rasa rayuka sanadiyyar ambaliyar ruwa da zaftarewar laka da aka samu wacce ta yi ajalin daririwan mutane.
-
Ana Dakon Sakamakon Zaben Shugaban Kasa A Angola
Aug 24, 2017 10:21Al'umma a Angola na ci gaba da dakon sakamakon zaben shugaban kasar da aka kada kuri'asa a jiya Laraba.
-
Yau Ne Za'a Gudanar Da Zaben Shugaban Kasa A Kasar Angola
Aug 23, 2017 00:55A yau ne ake sa ran al’ummar kasar Angola za su kada kuri’ar zaben 'yan majalisar kasar da zai share fagen zaben sabon shugaban kasar wanda zai maye gurbin shugaba Jose Eduardo Dos Santos wanda ya shafe kimanin shekaru 38 yana mulkin kasar.
-
WHO Ta Yi Gargadin Yaduwar Cututtuka A Saliyo
Aug 22, 2017 06:27Hukumar lafiya ta duniya WHO, ta yi gargadin cewa, akwai yiwuwar yaduwar wasu cututtuka kamar amai da gudawa da zazzabin sauro a Saliyo, bayan iftiila'in ambaliyar ruwa da zaftarewar laka da ta auku a makon da ya gabata a kasar, wacce ta hadassa mutuwar mutane 500.
-
Sudan: Jam'iyyun Siyasar Kasashen Afirka Sun Yi Taro A Birnin Khartum.
Aug 20, 2017 13:42Wakilan jam'iyyun siyasa 32 ne da su ka fito daga kasashen Afirka daban-daban su ka yi taron domin karfafa alakar aiki a tsakaninsu.
-
Sharhi:Kokarin HKI Na Samun Gindin Zama A Nahiyar Afirka
Aug 20, 2017 00:52A kokarinta na fita daga cikin halin kadaici, haramcecciyar kasar Isra'ila na kokarin fadada alakarta da kasashen nahiyar Afirka, dangane da wannan batu, magabatan birnin tel-aviv suka kudiri shirya wani taro mai taken zaman kasashen Afirka da Isra'ila cikin watan OKtoba mai zuwa a kasar Togo.
-
Ran-Gadin Shugaba Al'Sisi A Wasu Kasashen Afirka
Aug 19, 2017 06:40A ci gaba da ran gadin da yake a wasu kasashen Afirka, shugaban kasar Masar Abdel Fattah Al-Sissi, ya gana da takwaransa na Chadi, Idriss Deby Itno jiya a birnin N’Djamena.
-
Mali : An Jingine Shirin Zaben Jin Ra'ayin Al'umma
Aug 19, 2017 06:39Shugaban Ibrahim Bubakar Keita na Mali na sanar da dage shirin zaben jin ra'ayin al'ummar kasar kan yiwa kundin tsarin mulkin kasar kwaskwarima.
-
Nakiya Ta Kashe Sojojin Burkina Faso Uku
Aug 18, 2017 06:48Rahotanni daga Burkina faso na cewa sojojin kasar uku ne suka rasa rayukansu a yayin da motarsu ta taka nakiya a lardin Turonata dake karamar hukumar Tongomayel dake yankin Sahel a arewacin Wagadugu babban birnin kasar.
-
RD Congo : Zabtarewar Kasa Ta Yi Ajalin Mutum 40
Aug 17, 2017 06:15Rahotanni daga Jamhuriya Demukuraddiyar Congo, na cewa mutane arba'in ne suka rasa rayukansu sakamakon zaftarewar kasa da aka samu a wani kauyen masinta a Ituri dake arewa maso gabashin kasa.