-
ICC : Dan Jihadi, Zai Biya Diyya A Timbuktu
Aug 17, 2017 06:01Kotun hukunta mayan laifuka ta duniya cewa da ICC, ta ce dan jihadin nan na Mali Ahmad al Faqi al Mahdi zai biyan diyya ta Yuro miliyan biyu da dubu dari bakwaiu saboda lalata wurare masu tarihi a birnin Timbuktu.
-
Yawan 'Yan Gudun Hijira Sudan Ta Kudu Ya Kai Miliyan Guda A Uganda
Aug 17, 2017 04:29Hukumar kula da kaurar bakin haure ta MDD ta fitar da alkalumen dake cewa, yawan 'yan gudun hujira Sudan ta kudu a kasar Uganda ya kai miliyan guda.
-
Odinga Ya Ce Zai Daukaka Kara Kan Sakamakon Zaben Shugaban Kasar Kenya
Aug 17, 2017 01:08Jagoran ‘yan adawar kasar Kenya wanda kuma ya sha kaye a zaben shugaban kasar da aka gudanar Raila Odinga ya bayyana cewa zai daukaka kara a kotun koli ta kasar kan sakamakon zaben shugabancin kasar da aka sanar inda shugaba mai ci Uhuru Kenyatta ya lashe.
-
An Fara Zaman Makoki Na Mako Guda A Kasar Saliyo
Aug 16, 2017 14:47Gwamnatin kasar Saliyo ta sanar da zaman makoki na maku guda domin jimamin mutanen da suka rasu a ambaliyar ruwa.
-
Ambaliyyar Ruwa Ta Yi Ajalin Mutum 312 A Saliyo
Aug 15, 2017 01:58Bayanai daga Saliyo na cewa a kalla mutane 312 ne suka rasa rayukansu a ibtila'in ambaliyar ruwa da zabtarewar kasa da laka data biyo bayan ruwan sama tamakar da bakin kwarya da aka samu a Freetown babban birnin kasar.
-
An Kashe Mutum 9 A Jerin Hare-hare Kan Sansanin MDD A Mali
Aug 15, 2017 01:57Rahotanni daga Mali na cewa mutane tara ne suka rasa rayukansu a wasu tagwayen hare-haren 'yan bindiga a sansanin tawagar kiyaye zaman lafiya ta MDD a Mali.
-
Fao: Gargadi Akan Fari A Gabacin Nahiyar Afirka
Aug 14, 2017 14:24Hukumar abinci ta duniya( fao) ta yi gargadi akan karuwar mutanen da suke mutuwa saboda fari a gabacin nahiyar Afirka.
-
Odinga Ya Ki Amincewa Da Shan Kaye, Yayi Kira Zuwa Ga Yajin Aiki
Aug 13, 2017 12:34Madugun 'yan adawan kasar Kenya Raila Odinga ya ki amincewa da kayen da ya sha a zaben shugaban kasar da aka gudanar yana mai kiran magoya bayansa da su fara yajin aiki don matsin lamba har sai an nada shi a matsayin shugaban kasa.
-
Ana Ci Gaba Da Dakon Sakamakon Zaben Shugaban Kasa A Kenya
Aug 11, 2017 13:43Al'ummar a Kenya na ci gaba da dakon sakamakon zaben shugaban kasar da aka kada kuri'arsa a ranar Talata data gabata.
-
Masar : Hadarin Jiragen Kasa Biyu Ya Yi Ajalin Mutum A kalla 36
Aug 11, 2017 11:06Hukumomin kiwon lafiya a Masar sun ce a kalla mutane 36 ne suka rasa rayukansu a yayin da wasu jiragen kasa biyu sukayi taho mu gama a arewacin kasar.