-
Kasashe 25 Na Afrika Na Tattaunawa Kan Yaki Da 'Yan Fashin Teku
Aug 10, 2016 01:22Kwararru da masana daga kasashe 25 na kungiyar kula da yankunan teku na Afrika ta yamma da ta tsakiya (OMAC), na halartar wani taro a Lome babban birnin kasar Togo domin dakile yawaitar yin fashi a teku.
-
DRC : An Soke Izinin Wata Mai Bincike Ta HRW
Aug 10, 2016 01:05Gwamnatin Jamhuriyar Dimokaradiyar Congo ta hana wata mai bincike kan keta hakkin bil Adama ci gaba da gudanar da aikinta a kasar.
-
An Bindige Sama Da Masu Zanga-Zanga 90 A Kasar Habasha
Aug 08, 2016 13:47Shaidun gani da ido da kuma majiyoyin 'yan adawa a kasar Habasha (Ethiopia) sun bayyana cewar jami'an tsaron kasar sun bindige sama da mutane 90 a yayin da suke gudanar da zanga-zanga a yankunan Oromiya da Amhara da ke kasar.
-
Shugaban Kasar Ivory Coast Ya Yi Ahuwa Wa Fursunoni 3,000 Da Ake Tsare Da Su A Gidan Kurkuku
Aug 07, 2016 06:38Shugaban kasar Ivory ya yi ahuwa ga fursunoni fiye da 3,000 da ake tsare da su a gidan kurkuku saboda murnar cikan shekaru 56 da samun 'yancin kan kasar.
-
Akalla Mutane 7 Sun Rasa Rayukansu A Zanga-Zangar Kyamar Gwamnati A Habasha
Aug 07, 2016 00:48Rahotanni daga kasar Habasha sun ce akalla mutane 7 ne suka rasa raukansu a wata taho mu gama da aka yi tsakanin dubban masu zanga-zangar adawa da gwamnatin kasar da kuma jami'an tsaro a jiya Asabar.
-
Gyaran Fuska A Cikin Rundunar Sojin Kasar Ivory Coast
Aug 07, 2016 00:48Ma'aikatar tsaro a kasar ivory Coast ta sanar da cewa ta fara gudanar da wani shiri na yin gyaran fuska a cikin ayyukan rundunar sojin kasar.
-
EU Ta Samar Da Wani Tallafin Jin Kai Ga Kasashen Nijeriya, Nijar da Kamaru
Aug 06, 2016 13:34Kwamitin kungiyar tarayyar Turai (EU) ya samar da wani karin tallafin jin kai na kudin Euro miliyan 12.5 ga kasashen Najeriya, Nijar da Kamaru da wadansu al'ummomin su suka tagaiyara saboda mastala boko Haram.
-
Habasha : An Cafke Masu Zanga-zanga Da Dama
Aug 06, 2016 11:21Rahotannin daga Habasha na cewa 'yan sanda sun cafke mutane da dama da kuma lakadawa wasu duka a lokacin da suka fito zanga-zanga yau Asabar a babban dandalin birnin Addis Ababa domin nuna kin jinin gwamnati.
-
Fatan Kasashen Afirka Na Kawo Karshen Rikicin Cikin Gida
Aug 06, 2016 01:04Jami'an Tsaro Na Kasashen Afirka 51 Sun yi Taro A Birnin Kigali Na Rwanda.
-
'Yan Adawa A Chadi Sun Sha Alwashin Gudanar Da Zanga-Zanga Duk Da Hanin Gwamnati
Aug 06, 2016 00:45'Yan adawa a kasar Chadi sun sanar da aniyarsu ta gudanar da gagarumar zanga-zangar kin jinin gwamnatin kasar a yau din nan Asabar da kuma gobe Lahadi duk kuwa da haramta musu hakan da gwamnatin kasar ta yi bisa hujjar cewa hakan yayi kusa da lokacin da ake shirin rantsar da shugaban kasar Idriss Deby a ranar Litinin mai zuwa.