-
Shugaba Buhari Ya Bukaci 'Yan Nijeriya Da Su Kara Hakuri Da Gwamnatinsa
May 29, 2016 10:37Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya yabi 'yan kasar saboda irin hakuri da juriyar da suka nuna tsawon shekara guda na mulkinsa duk kuwa da matsalolin da ake fuskanta yana mai kiransu da su kara hakuri da shirin gwamnatin nasa da gyara kasar.
-
Tsegerun Niger-Delta sun sake fasa bututan Mai
May 29, 2016 06:38A karo na Uku cikin mako guda, Tsegerun Niger Delta Avengers dake kudancin Najeriya, sun sake kai hare-hare kan rijiyoyi da bututan man feturin kasar, lamarin dake sake nakasa tattalin arzikin kasar.
-
Najeriya : An Sake Kaiwa Bututun Mai Hari
May 29, 2016 01:05A Najeriya an sake kaiwa wani bututun mai a yankin Neja Delta dake kudancin kasar hari, wanda ya kasance wani hari na uku a cikin mako guda a yankin mai arzikin man fatur a kasar.
-
Sojojin Nigeria Sun Kubutarda Mutane 11,600 Daga Hannun Boko Haram
May 28, 2016 09:53Shugaban tarayyar Nigeria Muhammadu Buhari ya bayyana cewa sojin kasar sun kubutar da yan Nigeria kimani 11,600 daga hannun kungiyar Boko Haram tun lokacinda ya hau kan kujerar shugabancin kasar shekara guda da ta gabata
-
Lauyoyin Sheikh Zakzaky Sun Kai Karar Gwamnati A Kotu
May 27, 2016 11:23Tawagar lauyoyi masu kare Sheikh Ibrahim Zakzaky karkashin jagorancin San Femi Falana, sun shigar da kara da ke neman a saki malamin wanda ake tsare da shi ba tare da gurfanar da shi a gaban kuliya ba tsawon watanni fiye da 5, inda suka ce hakan ya saba wa dukkanin dokoki.
-
Taron Koli Kan Harkar Tsaro A Najeriya
May 27, 2016 14:45A Najeriya, A ranar 26 ga watan Mayu nan ce aka kammala taron koli na kasar kan harkar tsaro na shekara 2016.
-
An Samu Tashin Farashin Mai A Kasuwar Mai Ta Duniya
May 27, 2016 00:41Rahotanni sun bayyana cewar a karon farko a shekarar 2016 an sami tashin farashin man fetur zuwa dalla 50 kan kowace gangar danyen man hakan kuwa ya biyo bayan yawaitar bukatarsa ne a kasashen duniya.
-
Gwamnatin Nigeria Zata Gabatar Da Wani Shiri Don Rage Radadin Da Mutane Suke Fama A Kasar
May 26, 2016 01:04Gwamnatin tarayyar Nigeria ta bayyana cewa zata samar da wasu shirye shirye na rage radadin da talakawan kasar suke fama da su sanadiyyar karin farashin makamashi a kasar.
-
Tsagerun Niger Delta Sun Dauki Nauyin Hare Hare Na Baya Bayan Nan A Yankin
May 26, 2016 01:03Wata kungiya ta tsagerun Niger Delta a kudancin Nigeria ta dauki alhakin tada boma bomai kan bututun kamfanin hakar mai na Chevron a yankin
-
Nigeria Ta Yi Kasa A Hasashen Tsawon Rai Wanda Hukumar Lafiya Ta Duniya Ta Fitar
May 24, 2016 13:00Rahoton hukumar lafiya ta duniya kan hasashen tsawon rayuwar mutane a kasashe daban daban na duniya ya nuna cewa tarayyar Nigeria tana daga cikin kasashe 7 masu karancin shekaru na rayuwa.