Lauyoyin Sheikh Zakzaky Sun Kai Karar Gwamnati A Kotu
May 27, 2016 11:23 UTC
Tawagar lauyoyi masu kare Sheikh Ibrahim Zakzaky karkashin jagorancin San Femi Falana, sun shigar da kara da ke neman a saki malamin wanda ake tsare da shi ba tare da gurfanar da shi a gaban kuliya ba tsawon watanni fiye da 5, inda suka ce hakan ya saba wa dukkanin dokoki.
kana lauyan San Femi Falana ya nemi da a biya Sheikh Zakzaky da matarsa da ake tsare da su ba bisa doka ba, diyya ta Naira bilyan biyu.
ga rahoton Muhammad Sani Abubakar
Tags