Guinea Conakry: Zanga-zangar Kin Amincewa Da Sakamakon Zabe
Feb 26, 2018 15:35 UTC
Mazauna babban birnin kasar ta Guinea Conakry sun shiga zaman dirshen da kuma gudanar da Zanga-zanga domin kim amincewa da sakamakon zabe
Kamfanin dillancin labarun Faransa ya ce; Dubban mutane ne a birnin Conakry suka shiga Zanga-zangar nuna kin amincewa da sakamakon zaben biranen da aka gabatar.
Masu Zanga-zangar sun rika kona tayoyi a manyan tituna tare da hana kai da komowar mutane.
Kungiyoyin ma'aikata da kuma 'yan hamayyar siyasa suna zargin cewa an yi magudi a cikin zaben da aka gudanar a ranar 4 ga watan Febrairu.
Jam'iyyun adawa sun yi barazanar fadada Zanga-zangar tasu zuwa dukkanin bangarorin kasar.
Tags