Jami'an Tsaron Tanzaniya Sun Kama Madugun 'Yan Adawar Kasar
Mar 28, 2018 08:11 UTC
Ma'aikatar shari'ar Tanzaniya ta sanar da cewa: Jami'an tsaron kasar sun kame madugun 'yan adawar Tanzaniya.
Ma'aikatar shari'ar Tanzaniya ta sanar da cewa: Jami'an tsaron Tanzaniya sun kame madugun 'yan adawar kasar Freeman Mbowe tare da wasu mukarrabansa guda biyar a jiya Talata kan zargin kokarin kunna wuta rikici da tarzoma a kasar.
Majiyar ma'aikatar shari'ar ta kara da cewa: Ana zargin Freeman Mbowe na jam'iyyar Party for Democracy and Progress da yin furucin tada tarzoma a lokacin gudanar da zanga-zangar adawa a ranar 16 ga watan Fabrairu a kokarin da suke yi na kawo karshen gwamnatin John Magufuli.