Yansanda Da Yan Adawa Sun Kara A Kasar Madagaska
Yansanda ya yan adawa a birnin Antananarivo na kasar Madagascar sun kara a lokacinda yan sanda suka yi kokarin tarwatsa wata zanga-zangar lumana wacce yan adawar suka shirya don nuna rashin amincewarsu da kafa wasu dokoki wadanda zasu hada yan takararsu tsayawa zaben shugaban kasa nan gaba a cikin wannan shekara.
Tashar talabijon ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa daruwan yan adawa ne, daga ciki har da yan majalisar dokokin kasar ta Madagascar suka fito kan tituna a safiyar yau asabar don nuna rashin amincewarsu da wasu dokokin da majalisar dokokin kasar ta amice da su, wadanda a ganinsu wani shinge ne suka dorawa dan takararsu, kuma tsohon shugaban kasar Mark Ravalomanana tsayawa takarar shugabancin kasar .
Wani dan majalisar dokokin kasar wanda ya ke cikin masu zanga-zangar, paul Bert Rahasimanana, ya ce dole shugaban kasar Hery Rajaonarimampianina ya sauka don suna aikinsu ya aiko masu, a matsayinsu na yan majalisa amma sai ya aiko masu da yan sanda wadanda suka fesa masu teargas. Majiyar yansanda ta tabbatar da mutuwar mutum guda da kuma jikita wasu 16.