An Karrama Sashen Hausa Na Radiyo Iran A Nijar
Jun 24, 2018 09:36 UTC
Kungiyar Marubuta ta kasa a Nijar #ASAUNIL ta karrama wasu gidajen kasa da kasa dake watsa shirye shiryen Hausa da lambar yabo bisa gudun muwar da suke bayar wa wajen bunkasa harsunan #Afirka musamman harshen Hausa.
Sashen Hausa na Radiyon Iran ma ya samu irin wannan lambar yabo daga kungiyar #ASAUNIL.
Sauren gidajen radiyoyin sun hada da BBC, VOA, DW , RFI da CRI.
Wakiliyarmu a Yamai, babban birnin Jamhuriya Nijar, Nana Zainabu Amadu ce ta wakilci sashen Hausa na Radiyo Iran, wajen karbar lambar yabon.