Wani jirgin Fasinja Ya fadi A Kasar Afrika Ta Kudu
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i32276-wani_jirgin_fasinja_ya_fadi_a_kasar_afrika_ta_kudu
Faduwar wani jirgin sama a kasar Afrika ta kudu ya yi sanadiyyar mutuwar mutun akalla guda sannan wasu 20 suka ji rauni.
(last modified 2018-08-22T07:02:05+00:00 )
Jul 11, 2018 02:35 UTC
  • Wani jirgin Fasinja Ya fadi A Kasar Afrika Ta Kudu

Faduwar wani jirgin sama a kasar Afrika ta kudu ya yi sanadiyyar mutuwar mutun akalla guda sannan wasu 20 suka ji rauni.

kamfanin dillancin labaran IRNA na kasar Iran ya nakalto hukumar bada agajin gaggawa ta kasar Afrika ta kudu tana fadar haka , ta kuma kara da cewa jirgin saman ya fadi ne a jiya talata kusa da tashar jiragen sama na Wonderboom a cikin birnin Protoria babban birnin kasar.

Akwai yiyuwan yawan wadanda suka rasu rayukansu ya karu don wasu daga cikin wadanda suka ji rauni suna cikin mummunan hali. 

Wadanda suka ganewa idanunsa faduwar jirgin sun bayyana cewa kafin faduwar jirgin, injinsa ya kama da wuta. Majiyar gwamnatin kasar ta bayyana cewa za'a fara gudanar da bicnike don gano musabbin faduwar jirgin.