Shugaban China Na Ziyara A Afrika
A jiya asabar shugaban kasar China Xi Jinping yafara ziyarar aiki na mako guda a wasu kasashen Afira inda ya fara da birnin Dakar na kasar Senegal.
Wannan ziyara dai ita ce karo na uku da shugaba Xi Jinping ke gudanar da ita a Afirka a matsayinsa na shugaban kasa, inda bayan da ya gana shugaban Macky Sall a birnin Dakar, ya wuce zuwa birnin Kigali na Rwanda inda zai gana da shugaba Paul Kagame, sannan a ranar Laraba ya wuce zuwa Afirka ta Kudu domin halartar taron kasashen duniya masu samun habakar tattalin arziki wato Brics a birnin Johanneshurg.
Ziyarar Xi dai na zuwa ne a daidai lokacin da Chinan ke fuskantar gagarumar hamayya a fannin kasuwanci daga gwamnatin Shugaba Donald Trump na Amirka, wanda gwamnatinsa ba ta damu sosai da kulla alaka da nahiyar ta Afirka ba, yankin da ke zaman na biyu mafi yawan al'umma a duniya.