An Hana Wani Babban Dan Adawa A Kasar Congo Shiga Kasar
Jami'an tsaron kan iyaka na kasar DMC Kongo sun hana Moise Katumbi hamshakin mai kudi kuma tsohon gwamnan lardin Katanga na kasar shiga kasarsa a jiya jumma'a.
Kamfanin dillancin labaran Reuters ya nakalto Katumbi yana fadar haka a shafinsa na tweeter, ya kuma kara da cewa gwamnatin kasarsa ta hana shi tafiya zuwa kasar da jirgin sama kuma ta hana shi shiga kasar daga kasar Zambia a jiya jumma;a/
Moise Katumbi ya ce yana son isa kasar kafin 8 ga watan Augusta don shigar da takardunsa na neman takarar shugabancin kasar wanda za'a gudanar a karshen wannana shekara.
Katumbi yana gudun hijiran radin kansa a kasashen waje tun shekara ta 2016 bayan da aka zarge shi da an-mundaha da kuma wasu laifuffuak.
Jami'an tsaron kasar Congo sun bayyana cewa za'a kama shi idan ya taka kasar.