'Yan Adawa Sun Gudanar Da Gagarimin Gangami A Kasar D/Congo
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i33401-'yan_adawa_sun_gudanar_da_gagarimin_gangami_a_kasar_d_congo
Duban mutane sun amsa kiran 'yan adawa a kinshasa babban binrnin kasar Demokaradiyar Congo.
(last modified 2018-09-30T02:58:05+00:00 )
Sep 30, 2018 02:58 UTC
  • 'Yan Adawa Sun Gudanar Da Gagarimin Gangami A Kasar D/Congo

Duban mutane sun amsa kiran 'yan adawa a kinshasa babban binrnin kasar Demokaradiyar Congo.

Kamfanin dillancin labaran kasar Faransa ya habarta cewa a jiya asabar dubun dubatan mutane ne suka amsa kirar shugabanin 'yan adawa a wani taron gangami a aka gudanar a birnin Kinshasa, wanda ya samu halarta 'yan takarar shugaban kasa 4.

A yayin da yake gabatar da jawabi, Jean-Pierre Bemba da hukumar zaben kasar ba ta tattance takararsa ba, ya gargadi gwamnatin Joseph Kabila a kan duk wani yunkuri na magudi a zaben shugaban kasar da za a yi karshen wannan shekara da muke ciki.

Har ila yau 'yan adawar sun nuna rashin amincewarsu da shirin gwamnati na samar da wasu motoci da za a kada kuri'a a cikinsu, inda suka bayyana hakan da cewa wani yunkuri ne na gudanar da magudi a zaben.

Kundin tsarin milki na kasar ta Congo ya haramtawa Shugaba Joseph Kabila sake tsayawa takara a karo na uku, inda ya bayyana Emmanuel Ramazani Shadary tsohon ministan cikin gida na kasar a matsayin dan takararsa.

A ranar 23 ga watan Dicembar 2018 ne za a gudanar da zaben Shugaban kasa a jamhoriyar Demokaradiyar Congo.