Rikicin Kabilanci Ya Salwanta Rayukan Mutum 44 A Habasha
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i33454-rikicin_kabilanci_ya_salwanta_rayukan_mutum_44_a_habasha
Akalla mutane 44 ne suka rasa rayukansu sanadiyar rikicin kabilanci a yammacin kasar Habasha.
(last modified 2018-10-03T03:21:53+00:00 )
Oct 03, 2018 03:21 UTC
  • Rikicin Kabilanci Ya Salwanta Rayukan Mutum 44 A Habasha

Akalla mutane 44 ne suka rasa rayukansu sanadiyar rikicin kabilanci a yammacin kasar Habasha.

Majiyoyin kasar Ethiopia sun sanar a jiya Talata cewa a farkon makon nan wani  sabon rikicin kabilanci ya barke tsakanin mazauna yankunan Oromia da Benishangul-Gumuz a yammacin kasar, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar akalla mutum 44.

Rahoton ya ce rikicin ya fara ne a yayin da wasu 'yan bindiga da ba a san ko su waye ba suka hallaka shugabanin yankin Benishangul-Gumuz a yankin Oromia a yayin da suka isa yankin domin tattauna yanayin tsaro a yankunan biyu dake makwabtaka da juna.

A yayin wannan rikici, kungiyoyin matasan bangarorin biyu sun amfani da duwatsu, da sanduna gami da yukake wajen farwa junansu.

A cewar hukumomin yankin, wannan rikici dai ya tilastawa duban al'ummar yankin barin wuraren taruwa da wuraren ayyukansu, da gidajensu.

Rikici tsakanin mazauna yankunan biyu ya samo asali ne tun a shekarar 2015, bayan da aka kwacewa wasu manoma filayen nomansu a yankin.