An Dage Zaman Sauraren Shari'ar Sheikh Zakzaky
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i33477-an_dage_zaman_sauraren_shari'ar_sheikh_zakzaky
Kotun da ke sauraren shari'ar sheikh Ibrahim Zakzaky jagoran harkar musulunci a Najeriya ta sanar da dage zaman shari'ar har zuwa ranar 7 ga watan Nuwamba.
(last modified 2018-10-04T09:04:10+00:00 )
Oct 04, 2018 09:04 UTC
  • An Dage Zaman Sauraren Shari'ar Sheikh Zakzaky

Kotun da ke sauraren shari'ar sheikh Ibrahim Zakzaky jagoran harkar musulunci a Najeriya ta sanar da dage zaman shari'ar har zuwa ranar 7 ga watan Nuwamba.

Rahotanni daga Najeriya sun ce a yau ne 4 ga watan Oktoban 2018 ake gudanar da zaman sauraren shari'ar sheikh Ibrahim Zakzaky a garin Kaduna, sai dai kotun ta sanar da dage zaman sauraren shari'ar har zuwa 7 ga watan Nuwamba mai kamawa, bayan da masu shigar da kara suka bukaci hakan,

Masu shigar da karar dai sun gaya wa kotun cewa a yau ne shugaban kasa Muhammad Buhari zai ziyarci Kaduna, saboda dalilai na tsaro suka bukaci a dage zaman shari'ar, kuma kotu ta amince da hakan.

Gwamnatin jahar Kaduna ce dai ta shigar da karar a kan sheikh Ibrahim Zakzaky da mai dakinsa Malama Zinatu Ibrahim, da kuma Sheikh Yakubu Yahaya Katsina da kuma Malam Sanusi Abdulkadir, bisa zarginsu da kashe soja guda a lokacin da sojoji suka kai farmaki a kan gidan Sheikh Ibrahim Zakzaky a Zaria a cikin watan Disamban 2015.

Harkar musulunci ta zargi sojojin Najeriya da yin kisan gilla a kan mabiya Harkar su kimanin 1000 a lokacin farmakin da suka kai kan gidan Sheikh Zakzaky, yayin da su kuma sojoji suke cewa adadin bai haka ba.