Masar: An Kashe Kiristoci 7 A Wani Harin Ta'addanci
Rahotanni da suke fitowa daga Masar sun ce wasu 'yan bindiga ne su ka kai hari akan motar safa da take dauke da kirisitoci kibdawa.
Bakwai daga cikin mutanen sun mutu sai kuma wasu 14 da su ka jikkata.
Tashar talabijin din al-Mayadeen ta ambato limanin kiristoci kibdawa na yankin Minya yana cewa; An kai wa mutanen hari a lokacin da suke kan hanyarsu ta zuwa gundumar Suhaj.
Kamfanin dillancin labarun Reuters kuwa ya ce an kai harin ne a kusa da majami'ar Saint Samuel da take a gundumar Minya.
Kawo ya zuwa yanzu babu cikakken bayani akan wadanda su ka kai harin da kuma manufarsu.
A cikin shekaru biyu na bayan nan an kai irin wannan harin akan mabiya addinin kirista a cikin kasar ta Masar wanda ya ci rayukan fiye da mutane 100.
Masar na fama da matsalar ta'addanci da kungiyoyi masu dauke da makamai suke kai hare-hare.