Somaliya: An Sami Karuwar Wadanda Su Ka Rasa Rayukansu Sanadiyyar Harin Ta'addanci
Majiyar 'yan sanda a kasar ta Somaliya ta ce ya zuwa yanzu adadin wadanda su ka kwanta dama sanadiyyar harin ta'addancin da aka kai a birnin Magadishu a ranar juma'a, ya karu zuwa 50
Kungiyar al-Shabab ta dauki alhakin kai wanda baya ga wadanda su ka kwanta dama, ya kuma jikkata wasu mutane 58.
Wasu motoci ne guda biyu da aka makare da bama-bamai su ka tarwatse a kusa da Hotel din sahafi, sai kuma harin kunar bakin wake a gab da kofar shiga Hotel din.
Da akwai manyan jami'an gwmanatin Somaliya wadanda suke rayuwa a cikin wannan Hotel din da aka kai wa harin.
Kungiyar al-Shabab da ta kai harin dai tana a matsayin babbar barazanar tsaro ga kasar Somaliya da kuma sauran kasashen da suke makwabtaka da ita.
Daga 2011 zuwa yanzu hare-haren kungiyar sun ci dubban rayukan mutane a cikin gida da kuma waje.