Congo:Amurka Ta Rufe Ofishin Jakadancinta Kwanaki 4 A Jere
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i34269-congo_amurka_ta_rufe_ofishin_jakadancinta_kwanaki_4_a_jere
Kamfanin dillancin Labarun Faransa ya ce; An shiga kwana na 4 da Amurkan ta rufe ayyukan ofishin jakadancinta da yake a birnin kinshasha na Jamhuriyar Demokradiyyar Congo
(last modified 2018-11-29T03:23:50+00:00 )
Nov 29, 2018 03:23 UTC
  • Congo:Amurka Ta Rufe Ofishin Jakadancinta Kwanaki 4 A Jere

Kamfanin dillancin Labarun Faransa ya ce; An shiga kwana na 4 da Amurkan ta rufe ayyukan ofishin jakadancinta da yake a birnin kinshasha na Jamhuriyar Demokradiyyar Congo

Tun a ranar 29 ga watan Nuwamba da ake ciki ne dai Amurkan ta sanar da cewa; Ta sami bayanai kwarara da suke nuni da cewa za a kai wa gine-ginen Amurka harin ta'addanci.

A bisa wancan rahoton ne ta dakatar da ayyukan ofishin jakadancin har sai illa masha Allahu.

Wannan matakin na Amurka ya zo ne a daidai lokacin da kasar ta Demokradiyyar Congo take shirin gudanar da manyan zabuka a ranar 23 ga watan Disamba

Babu wani bayani da ya fito daga gwamnatin kasar ta Congo dangane da matakin na Amurka na rufe ofishin jakadancinta