An Tsawaita Dokar Ta Baci A Kasar Tunisiya
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i34339-an_tsawaita_dokar_ta_baci_a_kasar_tunisiya
Shugaban kasar ta Tunisiya ne ya sanar da tsawaita dokar ta baci da kasar take aiki da ita zuwa karin wata daya anan gaba
(last modified 2018-12-06T03:38:51+00:00 )
Dec 06, 2018 03:38 UTC
  • An Tsawaita Dokar Ta Baci A Kasar Tunisiya

Shugaban kasar ta Tunisiya ne ya sanar da tsawaita dokar ta baci da kasar take aiki da ita zuwa karin wata daya anan gaba

A wata sanarwa da ofishin shugaban kasar ta Tuniya ta fitar a jiya Laraba ya bayyana cewa; An tsawaita dokar ne daga juma'a 7 ga watan nan na Disamba zuwa 5 ga watan Janairu na 2019

Ofishin shugaban kasar ya ce; An dauki wannan matakin ne bayan tattaunawar da aka yi a tsakanin shugaban kasa da Pira minista da kuma shugaban majalisar dokokin kasar

A karon farko kasar ta Tunisiya ta fara aiki ne da dokar ta baci tun daga ranar 24 ga watan Nuwamba na 2015 bayan wani harin ta'addanci da aka kai wa motar safa mai dauke da sojoji.

A wancan harin an kashe mutane 38 da suka hada da 'yan sanda 12.

Kungiyar 'yan ta'adda ta Da'esh ta dauki alhakin kai wancan harin