'Yan Majalisar Sudan Na Kokari Ba Wa Shugaba Bashir Damar Yin Tazarce
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i34350-'yan_majalisar_sudan_na_kokari_ba_wa_shugaba_bashir_damar_yin_tazarce
Rahotanni daga kasar Sudan na nuni da cewa 'yan majalisar kasar sun goyi bayan wani shiri na yin kwaskwarima ga kundin tsarin mulkin kasar da zai ba wa shugaban kasar Umar Hasan al-Bashir damar yin tazarce a kan karagar mulkin kasar.
(last modified 2018-12-06T12:18:14+00:00 )
Dec 06, 2018 12:18 UTC
  • 'Yan Majalisar Sudan  Na Kokari Ba Wa Shugaba Bashir Damar Yin Tazarce

Rahotanni daga kasar Sudan na nuni da cewa 'yan majalisar kasar sun goyi bayan wani shiri na yin kwaskwarima ga kundin tsarin mulkin kasar da zai ba wa shugaban kasar Umar Hasan al-Bashir damar yin tazarce a kan karagar mulkin kasar.

Yayin da yake sanar da hakan, kakakin majalisar dokokin kasar ta Sudan Ibrahim Ahmed Omar ya ce ya sami wasikar da mafi yawa daga cikin 'yan majalisar suka sanya  wa hannu suna goyon bayan yin sauyi cikin kundin tsarin mulkin kasar da zai ba wa shugaba Bashir din damar yin tazarce a kan karagar mulkin kasar.

A bisa kundin tsarin mulkin na yanzu dai, shugaba Al-Bashir wanda ke mulkin kasar  ta Sudan tun  shekarar 1989 ba shi da damar tsayawa takarar shugabancin kasar bayan wa'adin mulkinsa ya  kare a shekara ta 2020, hakan  ne ya sanya 'yan majalisar suke son a yi gyaran fuska  wa kundin tsarin mulkin da zai ba shi damar sake tsayawa a zabe na  gaban.

Kasar Sudan din dai  tana fuskantar matsaloli na siyasa da tattalin arziki lamarin da ya sanya gwamnatin ta Bashir fuskantar zanga-zangogi daga  'yan adawa wadanda  suke kiransa da  ya  sauka daga karagar mulkin.