Libya: Kungiyar Da'esh Ta Dauki Alhakin Kai Hari A Birnin Tripoli
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i34573-libya_kungiyar_da'esh_ta_dauki_alhakin_kai_hari_a_birnin_tripoli
Kungiyar 'yan ta'addar ta fitar da wani bayani a jiya Talata da dare da a ciki ta bayyana cewa; ita ce ta kai hari akan ma'aikatar harkokin wajen kasar a birnin Tripoli
(last modified 2018-12-26T03:38:13+00:00 )
Dec 26, 2018 03:38 UTC
  • Libya: Kungiyar Da'esh Ta Dauki Alhakin Kai Hari A Birnin Tripoli

Kungiyar 'yan ta'addar ta fitar da wani bayani a jiya Talata da dare da a ciki ta bayyana cewa; ita ce ta kai hari akan ma'aikatar harkokin wajen kasar a birnin Tripoli

Da safiyar jiya Talata ne dai dai wasu mahara su 4 suka dumfari ginin ma'aikatar harkokin wajen kasar da ke birnin Tripoli, inda su ka tarwatsa kawukansu

Dukkanin maharan su uku sun halaka yayin da wasu mutane 9 su ka jikkata

Libya na fuskantar matsalar tsaro wacce ta samo asali tun 2011 da aka kifar da gwamnatin Mu'ammar Khaddafi ta hanyar tsoma bakin Amurka da kasashen turai

Bugu da kari har yanzu ana ci gaba da samun sabani a tsakanin bangarorin siyasar kasar da su ka kafa gwamnatoci biyu a cikin biranen Tubruk da kuma Tripoli. Gwamnatin hadin kan kasar da aka kafa a karkashin Fayez Suraj tana samun goyon bayan kasashen turai da su ka hada da Amurka, sai dai har yanzu ba ta shimfida ikonta a dukkanin fadin kasar ba.