An Fara Gudanar Da Zaben Shugaban Kasa A Congo
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i34609-an_fara_gudanar_da_zaben_shugaban_kasa_a_congo
Da safiyar yau ne aka bude rumfunan zabe a jamhuriyar dimukradiyyar Congo, domin gudanar da zaben shugaban kasa a kasar.
(last modified 2018-12-30T03:30:08+00:00 )
Dec 30, 2018 03:30 UTC
  • An Fara Gudanar Da Zaben Shugaban Kasa A Congo

Da safiyar yau ne aka bude rumfunan zabe a jamhuriyar dimukradiyyar Congo, domin gudanar da zaben shugaban kasa a kasar.

Kamfanin dilalncin labaran faransa ya bayar da rahoton cewa, jami'an hukumar zaben kasar ne suka fara kada kuri'unsu, kamar yadda kuma sauran jama'ar gari suka shiga cikin layuka a mazabu domin kada kuri'unsu.

Ana gudanar da zaben na yau ne dai bayan daga lokacin gudanar da shi har sau uku, inda za a zabi shugaban kasa wanda zai maye gurbin shugaba Joseph Kabila, inda 'yan takara uku za su fafata da juna.

Ana sa ran za a sanar da sakamakon zaben daga nan zuwa ranar 15 ga watan Disamba na shekara ta 2019 mai kamawa, kamar yadda kuma zababben shugaban kasar zai yi rantsuwar kama aiki a ranar 18 ga watan na Janairu.