Mahara Sun Kashe Mutane Fiye Da 30 A Tsakiyar Kasar Mali
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i34643-mahara_sun_kashe_mutane_fiye_da_30_a_tsakiyar_kasar_mali
Gwamnatin kasar Mali ta sanar a jiya Talata cewa wasu mutane masu dauke da makamai sun kai hari a kauyen Koulogon da yake a yankin Mopti a tsakiyar kasar
(last modified 2019-01-02T03:38:57+00:00 )
Jan 02, 2019 03:38 UTC
  • Mahara Sun Kashe Mutane Fiye Da 30 A Tsakiyar Kasar Mali

Gwamnatin kasar Mali ta sanar a jiya Talata cewa wasu mutane masu dauke da makamai sun kai hari a kauyen Koulogon da yake a yankin Mopti a tsakiyar kasar

Sanarwar ta gwamnati ta ci gaba da cewa; Mahran sun kashe fararen hula 37 da kuma jikkata wani adadi mai yawa

Bugu da kari maharan sun cinna wuta a cikin gidajen kauyen, tare da haddasa asarar dukiya mai yawa

kawo ya zuwa yanzu babu wata kungiya wacce ta dauki alhakin kai harin, sai dai wasu bayanai na nuni da cewa harin bai rasa nasaba da rikici na kabilanci

Tsakiyar kasar Mali yana fama da tashe-tashen hankula a cikin watannin bayan nan. Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana damuwarta akan abin da yake faruwa acikin yankin