Jam'iyya Mai Mulki A Sudan Ta Ki Amincewa Da Bukatar Wargaza Gwamnati
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i34655-jam'iyya_mai_mulki_a_sudan_ta_ki_amincewa_da_bukatar_wargaza_gwamnati
Jam'iyyar Sudan National Congress mai mulki a kasar Sudan ya yi watsi ta bukatar jam'iyyun adawar kasar na a wargaza gwamnati da majalisar dokokin kasar.
(last modified 2019-01-03T08:23:07+00:00 )
Jan 03, 2019 08:23 UTC
  • Jam'iyya Mai Mulki A Sudan Ta Ki Amincewa Da Bukatar Wargaza Gwamnati

Jam'iyyar Sudan National Congress mai mulki a kasar Sudan ya yi watsi ta bukatar jam'iyyun adawar kasar na a wargaza gwamnati da majalisar dokokin kasar.

Shafin yanar gizo na ARABIC 21 ya nakalto Abdul Rahaman Alkhidir shugaban banganen siyasa na jam'iyyar Sudan National Congress  yana fadar haka a jiya Laraba, ya kuma kara da cewa daukar wannan matakin yana dai-dai da juyin mulki a wajensa.

A ranar Talatan da ta gabata ce gamayyar jam'iyyun adawar kasar Sudan wacce ake kira "Natinal Change Front" , wacce kuma ta hada da jam'iyyar "Umma" wacce tsohon Firai ministan kasar Sadiq Almahdi yake jagoranta, ta fidar da wata sanarwa wacce ta bukashi shugaba Umar Hassan Albashir ya wargaza gwamnati da majalisar dokokin kasar don samar da hanyar fito daga matsalolin tsaro da tsadar kayakin da kasar ta fada ciki a yan makonnin da suka gabata.

Tun ranar 19 ga watan Dedcemban shekarar da ta gabata ce mutanen Sudan suke zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da tsadar kayakan aminci da bukatun yau da kullum a kasar, wanda kuma ya jawo mutuwar mutane da dama sanadiyar dirar mikiyan da jami'an tsaron kasar suka yi wa masu zanga-zangar.