Majalisar Dinkin Duniya Ta Yi Tir Da Mummunan Hari A Kasar Mali
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i34662-majalisar_dinkin_duniya_ta_yi_tir_da_mummunan_hari_a_kasar_mali
Kamfanin dillancin labarun Xinhua na kasar Sin ya ce; Rundunar MDD ta tabbatar da zaman lafiya a kasar ta Mali MINUSMA ta fitar da bayani a jiya laraba da a ciki ta yi Allah wadai da harin da aka kai a garin Mopti wanda ya ci rayukan mutane
(last modified 2019-01-03T15:39:53+00:00 )
Jan 03, 2019 15:39 UTC
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Yi Tir Da Mummunan Hari A Kasar Mali

Kamfanin dillancin labarun Xinhua na kasar Sin ya ce; Rundunar MDD ta tabbatar da zaman lafiya a kasar ta Mali MINUSMA ta fitar da bayani a jiya laraba da a ciki ta yi Allah wadai da harin da aka kai a garin Mopti wanda ya ci rayukan mutane

A kalla mutane 37  mafi yawancinsu mata da kananan yara  ne aka kashe a yayin harin da aka kai da safiyar ranar Talata

Bayanin ya ci gaba da cewa; Maharan da ba a tantance su ba sun kunna wuta a gidanen mutanen garin na Mopti wanda ya haddasa barnar dukiya da rayuka

Tsakiyar kasar Mali tana fuskantar rashin tsaro tun 2016 saboda fadace-fadace masu alaka da kabilanci. Fiye da mutane 500 ne aka kashe a cikin yankin a shekarar 2018 da ta wuce