Jam'iyyar Da Take Mulki A Congo Tana Shakku Kan Sakamakon Zabe
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i34754-jam'iyyar_da_take_mulki_a_congo_tana_shakku_kan_sakamakon_zabe
Jami'yyar mai mulki a kasar ta Jamhuriyar Demokradiyyar Congo " Common Front For Congo" ta ce tana da hakkin daukaka kara akan sakamakon zabe na farko da aka fitar
(last modified 2019-08-10T10:24:46+00:00 )
Jan 10, 2019 15:56 UTC
  • Jam'iyyar Da Take Mulki A Congo Tana Shakku Kan Sakamakon Zabe

Jami'yyar mai mulki a kasar ta Jamhuriyar Demokradiyyar Congo " Common Front For Congo" ta ce tana da hakkin daukaka kara akan sakamakon zabe na farko da aka fitar

Kakakin jam'iyyar mai mulki a kasar, Lambert Mende ya ce; Suna da hakkin daukar matakan sharia akan sakamakon farko na zaben shugaban kasar da hukumar zabe ta sanar

Jam'iyyar mai mulki ta tsayar da Emmanuel Ramazani Shadary ne a matsayin dan takararta da zai gaji shugaba Joseph Kabila idan ya ci zabe.

A yau alhamis ne hukumar zaben kasar ta Jamhuriyar Demokradiyyar Congo ta sanar da cewa; dan takarar jam'iyyar hamayya, Felix Tshisekedi ne ya lashe zaben shugaban kasar

An gudanar da zaben shugaban kasar ne ta jamhuriyar Demokradiyyar Congo a ranar 30 ga watan Disamba na shekarar 2018 da ta shude.

Wannan zai zama shi ne karon farko a tarihin kasar da farar hula zai karbi mulki daga farar hula ta hanyar zabe.

Shugaba Joseph Kabila ya hau kan karagar mulkin kasar ne tun bayan kashe mahaifinsa Laurence Kabila a 2001