An Kashe Mutane 8 A Rikicin Bayan Zaben Kasar Jamhuriyar Demokradiyyar Congo
Majiyar 'yan sandan kasar ta Jamhuriyar Demokraidyyar Congo ta bayyana cewa; Rikicin bayan zabe ya ci rayukan mutane 8 a yammacin kasar
Kamfanin dillancin labarun Faransa ya nakalto majiyar 'yan sandan na cewa; An kashe mutane 8 din ne a Kikwit da yake yammacin kasar
Majiyar ta kuma ci gaba da cewa; Wasu 'yan sanda 17 sun jikkata a sanadiyyar bata-kashi da masu Zanga-zanga
An gudanar da zaben shugaban kasar Jamhuriyar Demokradiyyar Congo ne a ranar 30 ga watan Disamba na 2018.
Sakamakon zaben ya bayyana Felix Tshisekedi a matsayin wanda ya lashe zaben
Wannan shi ne karon farko da farar hula zai mika wa farar hula mulki a tsawon tarihin kasar tun daga samun 'yanci 1960
Joseph Kabila ya hau karagar mulki ne a 2001 bayan kashe mahaifinsa Laurence Kabila.