Ana Ci Gaba Da Zanga-Zangar Kyammar Gwamnati A Sudan
Mutanen kasar Sudan suna ci gaba da zanga-zanga a wasu manya -manyann garuruwan kasar wadanda suka hada da Birnin Khartum babban birnin Kasar.
Kamfanin dillancin labaran Anatoliyo ya bayyana cewa a jiya Lahadi ma an gudanar da zanga-zanga a khartum babban birnin kasar da kuma garuruwan Al-Fashir, Al-Fai da kusa da birnin Port Sudan na bakin ruwa.
Labarin ya kara da cewa a birnin Port Sudan jami'an tsaro sun yi amfani da hayaki masu sa hawaye don tarwatsa masu zanga-zanga.
A dai-dai wannan lokacin ne jam'iyya mai mulkin kasar ta bayyana cewa idan har masu zanga zanga basu daina fifotuwa gwamnatu zata dauki matakin da yafi wanda suke dauka a halin yanzu.
Sai dai gamayyar jam'iyyun siyasar kasar da wasu kungiyoyi masu zanga kansu sun bada sa sanarwan cewa zasu fito gagarumin zanga-zanga a ranar Alhamis mai zuwa.