Mali : An Kai Hari Kan Tawagar Sojojin MINUSMA
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i34879-mali_an_kai_hari_kan_tawagar_sojojin_minusma
Majiyoyin tsaro daga Mali na cewa an kai wani hari kan tawagar wanzar da zaman lafiya ta MDD, ta MINUSMA a kasar Mali, wanda kuma ya yi sanadin mutuwar sojoji a kalla guda biyar.
(last modified 2019-01-20T07:31:17+00:00 )
Jan 20, 2019 07:31 UTC
  • Mali : An Kai Hari Kan Tawagar Sojojin MINUSMA

Majiyoyin tsaro daga Mali na cewa an kai wani hari kan tawagar wanzar da zaman lafiya ta MDD, ta MINUSMA a kasar Mali, wanda kuma ya yi sanadin mutuwar sojoji a kalla guda biyar.

An dai harin ne da sanyin safiyar yau Lahadi, a yankin a Aguelhok, dake arewacin kasar ta Mali a cewar majiyoyin.

Bayannan sun nuna cewa sojojin da suka rasa rayukansu a harin 'yan asalin kasar Chadi ne.

Wannan dai ba shi ne karon farko ba da ake kai hari kan tawagar wanzar da zaman lafiya ta MDD, ta MINUSMA a kasar Mali ba.