DR. Congo : Ranar Alhamis, Za'a Rantsar Da Tshisekedi
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i34917-dr._congo_ranar_alhamis_za'a_rantsar_da_tshisekedi
Majiyoyi daga bangaren gwamnatin DR Congo da makusantan zababen shugaban kasar, Félix Tshisekedi, sun tabbatar da cewa a gobe Alhamis ne za'a rantsar da sabon shugaban kasar.
(last modified 2019-04-27T09:55:10+00:00 )
Jan 23, 2019 07:18 UTC
  • DR. Congo : Ranar Alhamis, Za'a Rantsar Da Tshisekedi

Majiyoyi daga bangaren gwamnatin DR Congo da makusantan zababen shugaban kasar, Félix Tshisekedi, sun tabbatar da cewa a gobe Alhamis ne za'a rantsar da sabon shugaban kasar.

Mista Tshisekedi, zai maye gurbin shugaba Joseph Kabila, a bikin da za'a gudanar a fadar shugaban kasar.

Wannan dai kusan shi ne karo na farko da wani shugaban kasa zai mika mulki cikin ruwan sanyi a wannan kasa ta D.R Congo, tun bayan sanar da samun yancin kai na kasar a 1960.

Mista, Tshisekedi mai shekaru 55 na shirin zama shugaban kasar na biyar, inda zai gaji shugaba Kabila wanda ke shugabancin kasar tun shekara 2001, bayan ya gaji mulki daga mahaifisa Laurent-Désiré Kabila wanda aka kashe a lokacin.