Masar: An Kashe Kwamandojin 'Yan Ta'adda Biyu
Jan 28, 2019 04:12 UTC
Majiyar sojan Masar ta ce an kashe manyan kwamandojin 'yan 'ta'adda biyu ne a yankin Sina
Kamfanin dillancin Labarun Anatoli na Turkiya ya ambato kakakin sojojin Masar, Tamir al-Rufa'i' yana cewa; baya ga kwamandojin biyu, an kuma kashe wasu tarin 'yan ta'addar masu yawa
A yankin Sina da akwai kungiyoyin 'yan ta'adda da su ka kunshi Ansaru Baitul-Mukaddas da reshe ne na Da'esh, ko Isis. Kungiyar ta 'yan ta'addar sun sha kai hare-hare a cikin sassa daban-daban na kasar Masar
Yankin Sina ta Arewa a kasar Masar yana a matsayin tunga ta kungiyoyi daban-daban na 'yan ta'adda. "Yan ta'addar sun kashe sojoji masu yawa da kuma kai wa majami'u hare-hare.