Mali: An Kashe Sojojin Gwamnati Biyu
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i35011-mali_an_kashe_sojojin_gwamnati_biyu
Ma'aikatar tsaron kasar Mali ta bayyana cewa; An kashe sojojin biyu ne a wani hari da aka kai musu a kudancin kasar, tare kuma da jikkata wasu 10
(last modified 2019-01-30T15:54:35+00:00 )
Jan 30, 2019 15:54 UTC
  • Mali: An Kashe Sojojin Gwamnati Biyu

Ma'aikatar tsaron kasar Mali ta bayyana cewa; An kashe sojojin biyu ne a wani hari da aka kai musu a kudancin kasar, tare kuma da jikkata wasu 10

Kamfanin dillancin labarin faransa daga birnin Bamako ya ambato cewa; An kashe maharan da su ka kai wa sansanin sojan kasar a yankin Gao hari

A wani rahoto na watanni uku-uku da Majalisar Dinkin Duniya take fitarwa ta bayyana cewa; Fiye da rabin hare-haren da aka kai wa sojojin Mali, an kai su ne a cikin tsakiyar kasar da kuma arewacinta.

Kasar Mali ta fada cikin matsalar tsaro tun a cikin shekarar 2012.

Kasar Faransa wacce ta yi wa Mali mulkin mallaka ta aike da sojoji a kasar tun a 2013 domin fada da kungiyoyin da suke dauke da makamai masu fada da gwamnatin kasar

Majalisar Dinkin Duniya ta fitar da rahoto da a ciki ta bayyana cewa; A 2018 kadai rikice-rikicen kasar sun ci rayukan fararen hula 500