An Kashe Yan Bindiga 20 A Kasar Congo Demokradiyya.
Rundunar sojojin kasar Demokradiyar Kongo ta bada sanarwan cewa ta kashe yan bindiga 20 a gabancin kasar a wani sumamen da ta kai kan mabuyarsu a yankin.
Kamfanin dillancin labaran Anatoliya ya nakalto majiyar rundunar sojojin kasar na Kongo suna fadar haka a yau Lahadi.
Labarin ya kara da cewa Mayakan yan kungiyar "Patriotic Union for the Liberation of Congo" ko UPLC ne sojojin suka kashe a lokacin sumamen.
Kafin haka dai rundunar ta bayyana cewa mayakan kungiyar sun fara nuna wasu alamu na son tada hankali a yankin. An kafa kungiyar "Patriotic Union for the Liberation of Congo" a shekara ta 2018 da ta gabata, sannan tana cikin daruruwan kungiyoyin yan tawaye da suke tada hankali a gabacin kasar ta Kongo.
An dau shekaru fiye da 20 rabuwa da samun zaman lafiya a gabancin kasar democradiyyar Kongo.