Jiragen Yakin Faransa Sun Kai Hari A Kasar Chadi
Feb 05, 2019 04:35 UTC
A jiya Litinin ne jiragen yakin kasar Faransa su ka kai hari akan wata kungiya mai dauke da makamai a arewacin kasar Chadi
Ma'aikatar harkokin tsaron kasar Faransa ta ce ta kai harin ne akan wata kungiyar masu dauke da makamai na kasar Libya da su ka yi kuste cikin kasar
Bayanin ma'aikatar harkokin tsaron kasar ta Faransa ya ci gaba da cewa; Mutanen suna cikin ayarin motoci ne da su ka kai 40, kuma sa'aoi 48 da su ka gabaci kai harin an san da shigowar su cikin Chadi
Ma'aikatar harkokin tsaron kasar ta Faransa ta kuma ce; An kai harin ne dai bisa bukatar gwmanatin kasar Chadi
Faransa ta dade tana tsoma baki a harkokin cikin gidan nahiyar Afrika da sunan fada da ayyukan ta'addanci.