Najeriya: Akalla Mutane 39 Ne Suka Mutu A Zabukan Ranar Asabar
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i35365-najeriya_akalla_mutane_39_ne_suka_mutu_a_zabukan_ranar_asabar
Cibiyoyi da kungiyoyi masu zaman kansu da suka sanya ido a zaben Najeriya sun ce akalla mutane 39 ne suka rasa rayukansu a lokacin gudanar da zabukan.
(last modified 2019-02-25T11:40:52+00:00 )
Feb 25, 2019 11:40 UTC
  • Najeriya: Akalla Mutane 39 Ne Suka Mutu A Zabukan Ranar Asabar

Cibiyoyi da kungiyoyi masu zaman kansu da suka sanya ido a zaben Najeriya sun ce akalla mutane 39 ne suka rasa rayukansu a lokacin gudanar da zabukan.

Kamfanin dillancin labaran AFP ya bayar da rahoton cewa, a cikin bayanin da kungiyoyi da cibiyoyi kimanin 70 da suka sanya ido a zaben Nijaeriya suka fitar sun tabbatar da cewa, bisa ga bayanan da suka tattara, akalla mutane 39 ne suka rasa rayukansu a lokacin gudanar da zabukan.

Bayanin ya ce kimaninin rumfunan zabe dubu 120 ne a fadin Najeriya, kuma mafi yawansu babu isassun 'yan sanda da suke gudanar da ayyukan tsaro yadda ya kamata, duk kuwa da cewa a wurare da dama ba a samu hatsaniya ba, amma a wasu jahohin da suka hada da Rivers, Bayelsa da Delta, inda a cikin wadannan jahohi mutane 31 suka rasa rayukansu, mutane 8 an kashe su ne a cikin sauran wasu jahohin.

Sai dai a nasu bangaren jami'an 'yan sanda sun ce suna tsare da mutane kimanin 120 wadanda ake zarginsu da laifuka daban-daban a lokacin zaben, ad suka hada kisan mutane, sace akwatunan zabe da sauransu.