Yemen : Jiragen Saman Saudiyya Sun kashe Mutane Sama da 30
Feb 23, 2016 05:04 UTC
Wuraren da hare-haren suka shafa sun hada da lardinan al-Matmah da al-Khared dake yankin al-Jow.
Rahotanni daga kasar Yemen na cewa sama da mutane 30 ne suka rasa rayukan su sakamakon farmakin da jiragen kasar Saudiyyar ke ci gaba da kaiwa a kasar.
Galibin wadanda hare-haren suka rusa dasu fararen hula ne da suka hada da mata da yara kanana a cewar rahotannin.
Bayanai sun nuna cewa an kai hare-hare har sau biyar wanda suka hada da kan motocin jama'a da kuma motocin fasinja.
Wuraren da hare-haren suka shafa sun hada da lardinan al-Matmah da al-Khared dake yankin al-Jow.