Jordan : An Zartas Da Hukuncin Rataya Kan Mutane 15
Mar 04, 2017 07:11 UTC
Masarautar Jordan ta sanar da rataye wasu 'yan ta'adda da kuma masu muggan laifuka 15.
Da yake tabbatar da hakan kakakin gwamnatin kasar, Mahmoud al-Momani, ya ce an rataye mutanen ne a gidan yarin Suaga, dake kudancin birnin Amman.
Goma daga mutanen dai ana zarginsu da alaka da wata kungiyar 'yan ta'adda data kai hare hare a wurare da dama na kasar ciki harda kan cibiyar leken asiri da kuma kan jami'an tsaro da kuma kan offishin jadancin kasar a Bagadaza cikin 2003.
Sauren mutanen kuma ana zarginsu da aikata muggan laifuka ciki har da fyade.