Halakar Sojojin Hayar Saudiyya 10 A Lardin Ta'az Na Kasar Yamen
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i20146-halakar_sojojin_hayar_saudiyya_10_a_lardin_ta'az_na_kasar_yamen
Sojojin Yamen da dakarun Ansarullahi sun kashe sojojin hayar masarautar Saudiyya akalla 10 a lardin Ta'az da ke kudu maso yammacin kasar ta Yamen.
(last modified 2018-08-22T07:00:04+00:00 )
May 07, 2017 01:03 UTC
  • Halakar Sojojin Hayar Saudiyya 10 A Lardin Ta'az Na Kasar Yamen

Sojojin Yamen da dakarun Ansarullahi sun kashe sojojin hayar masarautar Saudiyya akalla 10 a lardin Ta'az da ke kudu maso yammacin kasar ta Yamen.

Majiyar rundunar sojin Yamen ta sanar da cewa: Sojojin Yamen da hadin gwiwar dakarun sa-kai na kasar sun kai wani harin kwanton bauna kan tawagar sojojin hayar masarautar Saudiyya a yankin Asifarah da ke lardin Ta'az a jiya Asabar, inda suka yi nasarar halaka sojojin akalla 10 tare da jikkata wasu adadi mai yawa.

A gefe guda kuma jiragen saman yakin masarautar Saudiyya sun yi luguden wuta kan yankin Annajibah da ke gabashin garin Al-Makha a lardin na Ta'az, inda suka rusa gidajen fararen hula amma babu cikakken labarin irin hasarar rayukan da hare-haren suka janyo.