Iraki: Isis ta kashe Fararen Hula 30 A Garin Al Huwaijah.
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i21478-iraki_isis_ta_kashe_fararen_hula_30_a_garin_al_huwaijah.
Tashar Telbijin din Somariyyah ta kasar Iraki ta ce; Mafi yawancin mutanen da Da'esh din ta kashe a garin na Huwaijah da ke gundumar Karkuk, mata ne da kananan yara.
(last modified 2018-08-22T07:00:16+00:00 )
Jun 19, 2017 06:26 UTC
  • Iraki: Isis ta kashe Fararen Hula 30 A Garin Al Huwaijah.

Tashar Telbijin din Somariyyah ta kasar Iraki ta ce; Mafi yawancin mutanen da Da'esh din ta kashe a garin na Huwaijah da ke gundumar Karkuk, mata ne da kananan yara.

Tashar Telbijin din Somariyyah ta kasar Iraki ta ce; Mafi yawancin mutanen da Da'esh din ta kashe a garin na Huwaijah da ke gundumar Karkuk, mata ne da kananan yara.

Anwar al-Asy, wanda daya ne daga cikin jagororin kabilar al Ubaid, ya cce;Daga 2014 zuwa yanzu,kungiyar 'yan ta'addar ta Da'esh ta kashe mutanen da su ka kai 1000.

A gefe daya, sojojin kasar ta Iraki da su ke fada da kungiyar Da'esh, sun kutsa cikin unguwanni na karshe da su ka saura a hannun kungiyar ta 'yan ta'adda a cikin birnin Musel. Kawo ya zuwa yanzu dai an kashe da dama daga cikinsu da kuma kame wasu.