Gwamnatin Algeria Ta Hana Wani Malamin Wahhabiyawa Shiga Kasarta
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i2194-gwamnatin_algeria_ta_hana_wani_malamin_wahhabiyawa_shiga_kasarta
Gwamnatin Kasar Algeria ta hana Mohammad Uraifi wani fitaccen
(last modified 2018-08-22T06:57:57+00:00 )
Mar 09, 2016 12:57 UTC
  • Mohammad Arifi -Malamin yan ta'adda
    Mohammad Arifi -Malamin yan ta'adda

Gwamnatin Kasar Algeria ta hana Mohammad Uraifi wani fitaccen

Gwamnatin Kasar Algeria ta hana Mohammad Uraifi wani fitaccen malamin wahhabiyawa dan kasar Saudia shiga kasarta. Jaridar Al-Ahram ta kasar Masar ta nakalto ministan harkokin addini na kasar Algeria Mohammad Isa yana fadar haka a yau Laraba ya kuma kara da cewa Mohammad Al-uraifi yana da fikra ta yan ta'adda don haka kasarsa ba zata amince masa shiga kasar.

Wasu majiyoyi sun bayyana cewa Mohammad Al-uraifi ne ya bada fatar "Jihadin Aure" ga kungiyoyin yan ta'adda da suke kisan mutane a kasashen Siria da Iraqi. Amma malaman ya musanta hakan.

Mohammad Al-Uraifi ya je kasar Algeria ne don halattan wani taron addini a daya daga cikin biranen kasar.

Kasar Saudia ce a gaba gaba wajen goyon bayan yan ta'adda a mafi yawan kasashen musulmi.