Limamin Masallacin Kudus Ya Jaddada Wajabcin Ci gaba Da Gwagwarmaya
Limamin masallacin Kudus Ikramah Sabry, ya fadi cewa; kafa kofar bincike da 'yan sahayoniya su ka yi a bakin masallacin Kudus keta hurumin masallacin ne.
Limamin masallacin Kudus Akramah Sabry, ya fadi cewa; kafa kofar bincike da 'yan sahayoniya su ka yi a bakin masallacin Kudus keta hurumin masallacin ne.
Sheikh Ikramah wanda jaridar al-ra'ay, ta kasar Kuwaiti ta yi hira da shi ya ci gaba da cewa; Kafa kofofin masu na'urorin bincike a masallacin kudus ba tare da tuntubar hukumar masallacin ba, yana a matsayin keta hurumin masallacin ne.
Sheikh Sabry ya jaddada cewa; daukar matakin kafa kofofin yana da alaka da siyasar cikin gida ta haramtacciyar kasar Isra'ila bayan da ake bincike Netanyaho akan handamar kudade.
A ranar juma'ar da ta gabata ne dai sojojin haramtacciyar kasar Isra'ila su ka hana masallacin kudus a karon farko a cikin rabin karni.