Hizbullah: 'Yan Ta'adda Na Shakar Lumfashinsu Na Karshe A Gabashin Lebanon
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i22596-hizbullah_'yan_ta'adda_na_shakar_lumfashinsu_na_karshe_a_gabashin_lebanon
Mayakan kungiyar Hizbullah na ci gaba da killace 'yan ta'adda da suka yi saura a cikin yankin Ta'al Nisab da ke cikin gundumar Jurud Arsal a kan iyakokin Lebanon da Syria, inda dakaruna na Hizbullah suka bayar da wa'adi ga 'yan ta'addan takfiriyyah da su mika kansu da makamansu, ko kuma a murkushe su da karfin bindiga.
(last modified 2019-08-10T10:24:46+00:00 )
Jul 26, 2017 07:29 UTC
  • Hizbullah: 'Yan Ta'adda Na Shakar Lumfashinsu Na Karshe A Gabashin Lebanon

Mayakan kungiyar Hizbullah na ci gaba da killace 'yan ta'adda da suka yi saura a cikin yankin Ta'al Nisab da ke cikin gundumar Jurud Arsal a kan iyakokin Lebanon da Syria, inda dakaruna na Hizbullah suka bayar da wa'adi ga 'yan ta'addan takfiriyyah da su mika kansu da makamansu, ko kuma a murkushe su da karfin bindiga.

Dakarun na Hizbullah sun tsarkake mafi yawan yankin daga 'yan ta'addan Jabhat Nusra da suke samun goyon wasu sarakunan larabawa gami da Isra'ila, tare da mika yankunan da suka tsarkake ga rundunar sojin kasar Lebanon.

A yau ne jagoran kungiyar ta Hizbullah zai gabatar da wani jawabi da kimanin karfe 8:30 na dare agogon Beirut dangane da halin da ak ci a ci gaba da tsarkake yankunan gabashin Lebanon daga 'yan ta'addan takfiriyyah.