Tawagar Kurdawa Daga Arbil Ta Isa Birnin Bagadaza
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i24167-tawagar_kurdawa_daga_arbil_ta_isa_birnin_bagadaza
Kurdawa Sun aike da tawaga zuwa Bagadaza kwanaki shida gabanin kuri'ar raba gardamar ballewa daga Iraki
(last modified 2018-08-22T07:00:43+00:00 )
Sep 19, 2017 07:53 UTC
  • Tawagar Kurdawa Daga Arbil Ta Isa Birnin Bagadaza

Kurdawa Sun aike da tawaga zuwa Bagadaza kwanaki shida gabanin kuri'ar raba gardamar ballewa daga Iraki

Kafafen watsa labarun Iraki sun ce da safiyar yau talata ne tagawar Kurdawan daga Arbil ta isa birnin Bagadaza domin ganawa da mahukuntan kasar akan batun kuri'ar raba gardamar ballewa daga Iraki.

A gefe daya, shugaban kasar ta Iraki "Fu'ad Ma'asum" ya ce warware sabanin da ke tsakanin Bagadaza da Arbil shi ne muhimman batun da ke gabansu.

A ranar asabar din da ta gabata, Pira minista Haydar Abadi, ya yi barazanar amfani da karfin soja akan Kurdawan idan har suka nace sai sun balle daga Iraki.

A ranar 25 ga watan nan na Satumba ne dai Kurdawan suka tsaida za su yi kuri'ar raba gardama ta ballewa daga Iraki.