Sojojin Iraki Sun Sauke Tutar Kurdawa Da Kudancin Karkuk
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i24913-sojojin_iraki_sun_sauke_tutar_kurdawa_da_kudancin_karkuk
Bayan da sojojin na Iraki suka sauke tutar ta Kurdawa sun maye gurbinta da ta Iraki.
(last modified 2018-08-22T07:00:49+00:00 )
Oct 14, 2017 08:19 UTC
  • Sojojin Iraki Sun Sauke  Tutar Kurdawa Da Kudancin Karkuk

Bayan da sojojin na Iraki suka sauke tutar ta Kurdawa sun maye gurbinta da ta Iraki.

Sojojin na Iraki sun fara taruwa a kusa da birnin Karkuk da ake da sabani akansa, tsakanin gwamnatin tsakiya da kuma ta yankin Kurdawa.

Majiyar tsaron kasar ta Iraki ta ce, matakin aikewa da sojojin shi ne shimfida ikon Bagadaza akan yankunan da ake da sabani akansu.

Kwamandan dakarun sa kai na "Hashd-sha'abi' Hadi al-amuri' ya yi kira ga mayakan kurdawa, na "Pesh-margah' da su fice daga yankunan da suke iko da su.

A baya, Mas'ud Barzani ya aike da mayakan Peshmarga zuwa yankin domin su kare yankin.