Hezbollah Ta Musunta Janyewa Daga Syria
Mar 16, 2016 08:50 UTC
kungiyar hizbollah ta kasar Lebonan ta musunta jitan-jitan cewa ta fara janye dakarun ta daga fagen daga a kasar Syria.
A wata tattauna da ya yi da mujallar Al'Qods Al'-Al-Arab, kakakin kungiyar Mohammad Afif ya ce babu wani kamshi gaskiya a cikin bayanai da wasu jaridu ke wallafawa na cewa sun fara janye dakarun su daga Syria.
Afiff ya kara da cewa kungiyar Hezbolla zata ci gaba da kasancewa Syria domin ci gaba da yaki da 'yan ta'adda a yankin Tadmor.