Yemen: Jiragen Yakin Saudiyya Sun Kashe Fararen Hula Da Dama
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i26195-yemen_jiragen_yakin_saudiyya_sun_kashe_fararen_hula_da_dama
Majiyar tsaron kasar Yemen ta ce a kalla mutane 23 ne suka kwanta dama sanadiyyar hare-haren da jiragen yakin na Saudiyya suka kai wa kasar a jiya asabar.
(last modified 2018-08-22T07:01:07+00:00 )
Dec 10, 2017 04:08 UTC
  • Yemen: Jiragen Yakin Saudiyya Sun Kashe Fararen Hula Da Dama

Majiyar tsaron kasar Yemen ta ce a kalla mutane 23 ne suka kwanta dama sanadiyyar hare-haren da jiragen yakin na Saudiyya suka kai wa kasar a jiya asabar.

Majiyar ta ci gaba da cewa; Jiragen yakin na Saudiyya sun kai hari ne a yankin Sha'aban, da garin Razih da suke a gundunar Sa'adah, wanda ya ci rayukan mutane 15.

Bugu da kari, jiragen yakin na Saudiyya sun kai wasu hare-haren a yankin "Bani Mu'az' da ke garin Sahhar a garin Sa'adha wanda ya dauki rayukan fararen hula 8.

A yankunan 'Dhibatul-Ismi' da 'Fara'a' da ke garin Kataf,  jiragen yakin na Saudiyya sun kai hare-hare har sau uku daya, bayan daya.

Kasar Saudiyya wacce take samun goyon bayan Amurka ta bude yaki akan Yemen tun a cikin watan Maris 2015, wanda kuma zuwa yanzu ya ci rayukan mutane fiye da 12,000 bisa kididdigar Majalisar Dinkin Duniya