Yeman : MDD Ta Zargi Saudiyya Da Kai Farmaki Kan Fararen Hula
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i2647-yeman_mdd_ta_zargi_saudiyya_da_kai_farmaki_kan_fararen_hula
MDD ta nuna damuwa matuka dangane da yadda Saudiyya ke ci gaba da kai farmaki kan fararen hula a kasar Yemen.
(last modified 2018-08-22T06:58:00+00:00 )
Mar 19, 2016 07:20 UTC
  • Yeman : MDD Ta Zargi Saudiyya Da Kai Farmaki Kan Fararen Hula

MDD ta nuna damuwa matuka dangane da yadda Saudiyya ke ci gaba da kai farmaki kan fararen hula a kasar Yemen.

kazalika MDD ta yi allawadai da yadda farmakin da kawacen da Saudiyya ke jagoranta ke shafar fararen hula wadanda basu ji basu gani ba, kamar yadda babban kwamishinan hukumar kare hakin bil adama ta MDD Zaeid Raad al-Hussain ya sanar.

wannann dai na zuwa bayan kazamin farmakin da Saudiyya ta kai ranar Talata data gabata a kasuwa Al-Khamees dake arewa maso yammacin kasar ta Yemen, inda fararen hula 106 galibi yara kanana suka rasa rayukan su.