Yemen: Sojoji Sun Kwace Garin al-Khoja Da ke Gundumar Hudaidah.
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i26795-yemen_sojoji_sun_kwace_garin_al_khoja_da_ke_gundumar_hudaidah.
Sojojin kasar Yemen da kuma dakarun sa kai na Ansarullah, sun sanar da kwace garin ne a yau alhamis.
(last modified 2018-08-22T07:01:12+00:00 )
Dec 28, 2017 15:33 UTC
  • Yemen:  Sojoji Sun Kwace Garin al-Khoja Da ke Gundumar Hudaidah.

Sojojin kasar Yemen da kuma dakarun sa kai na Ansarullah, sun sanar da kwace garin ne a yau alhamis.

A yayin kwace garin daga hannun yan koren Saudiyya, sojojin na Yemen sun kuma lalata motocin yaki masu sulke da kuma wasu kayan yaki.

A gefe daya, yan koren na Saudiyya da jiragen yakin na Saudiyya suke yi wa rakiya sun sha kashi a hannun "Ansarullah'  a korarin da suka yi na isa yankin al-qaeda.

Dakarun sa kai na Ansarullah sun lalata tankokin yaki da motoci masu sulke a arewacin Ta'iz.

Saudiyya da Hadaddiyar Daular Larabawa bisa goyon bayan Amurka suna yakar Yemen tun 2015 har zuwa yanzu. Dubban mutane ne suka rasa rayukansu sanadiyyar yakin.