Siriya Ta Musunta Yin Amfani Da Makamai Masu Guda
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i27557-siriya_ta_musunta_yin_amfani_da_makamai_masu_guda
Gwamnatin Siriya ta yi fatali da zargin da akewa dakarun kasar da amfani da makamai masu guba kan 'yan tawaye a kusa da birnin Damascos.
(last modified 2018-08-22T07:01:19+00:00 )
Jan 24, 2018 07:41 UTC
  • Siriya Ta Musunta Yin Amfani Da Makamai Masu Guda

Gwamnatin Siriya ta yi fatali da zargin da akewa dakarun kasar da amfani da makamai masu guba kan 'yan tawaye a kusa da birnin Damascos.

Haka zalika gwamnatin kasar ta kuma allawadai da zarge-zarge marar tushe da ake yi mata da amfanin da makamai masu guba.

A ranar Juma'a daga gabata ne kungiyar dake sa ido kan al'amuran kare hakkin bil adama a Siriya (OSDH) ta zargi dakarun gwamatin Siriya da amfani da makamai masu guba a yankin Ghouta da ke yammacin Damascos.

Siriya dai ta jima tana musunta zarge zargen da ake mata kan amfani da makamai masu guba, bayan da a cewar ta a 2013 ta amunce da bayyanawa da kuma mika makamanta masu guba bisa yarjejeniya da hukumar yaki da makamai masu guba.