Yemen: An Halaka 'Yan Koren Saudiyya A Gundumar Ta'iz
May 09, 2018 02:26 UTC
Sojojin Yemen sun kai harin da su ka shammati 'yan koren Saudiyya da ke gundumar Ta'iz a yankin Kudu maso yammacin kasar ta Yemen
Kafafenn watsa labarun Yemen sun ambaci cewa a yayin harin an kashe 'yan koren Saudiyya da dama da kuma jikkata wasu.
Wata majiyar sojan Yemen ta ce; mayaka 9 masu alaka da Abdu Rabbuh Mansur Hadi ne aka kashe a wani harin da aka kai musu a gundumar Sa'adha da ke arewacin kasar.
A lokaci guda kuma jiragen yakin Saudiyya sun kai wasu hare-haren a gundumar Ma'arib.
Saudiyya bisa cikakken goyon baya da kuma taimakon Amurka sun bude kai wa Yemen hari tun 2015, wanda kawo ya zuwa yanzu ya ci rayukan mutane 13,000.